Gwamnan jihar Nasarawa Umaru Al-Makura ya baiwa jami’an tsaro wa’adin kwana bakwai don kamo ‘yan bindigar da suka kashe mutum 16 a kauyen Numa Kochu da ke karamar hukumar Akwanga.
Gwamnan ya bayar da umarnin yayin ziyarar da ya kaiwa wadanda aka jikkata a babban asibitin Akwanga a jiya Talata.
Gwamna Al-Makura ya kara da cewa, jihar ta kasance cikin zaman lafiya a shekaru uku da suka wuce, don haka gwamnati ba zata lamunci barazanar rashin tsaro a yanzu ba.