✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ya kuke kallon salon mulkin Buhari da gwamnoni?

Ranar 29 ga watan Mayu shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da wasu gwamnonin kasar ke cika shekara daya a zangon mulkinsu su na biyu kuma na…

Ranar 29 ga watan Mayu shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da wasu gwamnonin kasar ke cika shekara daya a zangon mulkinsu su na biyu kuma na karshe.

Shin kun gamsu da kamun ludayin gwamnatin Shugaba Buhari a shekarar farkon wa’adinsa na biyu?

Wane gwamna kuke ganin ya ciri tuta?

Daga cikin gwamnonin akwai wadanda a wannan ranar suke cika shekara daya a mulkinsu karo na farko.

Masu cika shekara daya su ne gwamnonin jihohin Legas da Ogun da Oyo a yankin Kudu maso yamma.

Sai gwamnan jihar Zamfara daga Arewa maso yamma da kuma jihohin Borno, Yobe, Adamawa da Gombe a Arewa maso Gabas.

Cikonsu shi ne gwamnan jihar Nasarawa a Arewa ta tsakiya.

Ku fada mana ra’ayinku

Shin kun gamsu da salon mulkin Shugaba Buhari a shakarar farkon wa’adinsa na biyu?

Wane gwamna kuke ganin ya ciri tuta?