Hukumar da ke shirya jarrabawar shiga jami’a a Najeriya (JAMB) a yau Asabar ta fitar da sakamakon jarrabawar dalibai 1,792,719 cikin dalibai 1,826,839 da suka rubuta jarrabawar wannan shekarar ta 2019 jarrabawa (UTME). Adadin dalibai 1, 886,508 suka yi rijistar jarrabawar, kamar yadda Rijistaran hukumar JAMB Farfesa Is-haq Oloyede ya bayyanawa manema labarai a Abuja.
Ba a fitar da sakamakon wasu dalibai 34,120 saboda wasu dalilai.
Cikakken rahoton na nan tafe.