Shugaban Hukumar hana fasa kwauri ta Najeriya wato (Kwastam) Kanal Hameed Ali (mai ritaya), ya ce hukumar kwastan (NCS) ta bude shafin ta na intanet daga karfe 12:00 na safiyar yau Laraba domin baiwa masu sha’awar aiki da hukumar damar nuna sha’awar su ta cike gurbin ma’aikata 3,200.
Mukaddashin mataimakin Kwanturola Janar mai kula da sashen walwalar ma’aikatan, Sanusi Umar, wanda ya wakilci Kanal Hameed, ne ya bayyana hakan ne a jiya Talata, a Abuja.
Sanusi, ya qara da cewa, daukan sabbin ma’aikatan ya biyo bayan amincewar kwamitin zartar wa na gwamnatin tarayya. Za a bude shafin daukar ma’aikatan a cikin makonni uku, ta hanyar shiga shafin (vacancy.customs.gov.ng)