Hukumar Kula da Tsabtace Muhalli ta Jihar Katsina(SEPA) ta yi dacen shugaba. Tun lokacin da Alhaji Isah Sa’idu Barda ya zama Shugaban Hukumar aka samu ci gaba sosai a fannin tsabtace Jihar Katsina. Shigarsa ofis ke da wuya ya fara aiki wurjanjan wajen samar da wurare da kwama-kwamai inda jama’a za su rika zuba shara, sabanin kafin zuwansa inda ake zubar da ita barkatai. Ya kuma samar da wuraren yin ba-haya da wanka a cikin farashi mai sauki. Safe da rana ma’aikatan hukumar suna share titunan birnin jihar gami da yashe magudanun ruwa a kai-a kai.Da fatar jama’a za mu ba shi goyon baya domin ci gaba da wannan kokari da yake yi
Haruna Muhammad Katsina.Shugaban Kungiyar Muryar Jama’a. (07039205659)