✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jami’an kwastam sun bukaci a kammala aikin bakin iyaka

Jami’an kwastan  masu kula da  bakin iyakar  Najeriya da Jamhuriyar Benin sun bukaci a kammala  aikin  sabunta  bakin iyakar  da ke tafiyar  hawainiya, yau shekaru …

Jami’an kwastan  masu kula da  bakin iyakar  Najeriya da Jamhuriyar Benin sun bukaci a kammala  aikin  sabunta  bakin iyakar  da ke tafiyar  hawainiya, yau shekaru  biyu  ke nan da aka ba da  shi, kuma  sun ce  wannan na kawo  wa  aikinsu  cikas.
Da yake wa  taron manema  labarai  jawabi,  shugaban kwastam  mai kula da  bakin iyakar,  Kwanturola Othman Suleman  ya ce  rashin wadatattun  ofisoshi yana shafar aikinsu, kodayake  hakan bai sa  sun gaza wajen  gudanar  da  ayyukan nasu ba.
Kwanturola Othman ya ce  kudin  shigar  da  suka  samu  daga  farkon  wannan shekarar  zuwa  yanzu ya fi abin da suka  samu  a bara gaba daya. “Samun  nasarar  hakan ya  biyo  bayan  irin goyon  bayan  da muke samu  daga Kwanturola-Janar Abdullahi Dikko Inde da mukarabansa, wanda ba don haka  ba da Najeriya  ta rika  babbar asarar kudin shiga”. Inji shi.
Da ya  tabo dangantakar  hukumar  kwastan  da  sauran  jami’an tsaro  da ke  aiki  bakin iyakar  ta  jamhuriyar  Benin da Najeriya,  sai  ya ce dangantakar mai karfi ce domin  kowane  wata  suna  ganawa  tsakaninsu don kara  samar  da  dabarun gudanar da  ayyukansu  da hanyoyin inganta su,  musammam  ma kan yadda  za su  dakile  shigo da  makamai  ko kuma duk wani  mugun abu da zai cutar da kasa.
Ya ce suna ta kokarin samar da kyakkyawar dangantarsu da jami’an  tsaro na kasar Benin yadda za a gudanar da aiki kowace kasa ta amfana, musamman a fannin lamarin da ya shafi karuwar samun kudin shiga, hasali ma ga shi an samar musu  sabuwar na’ura  mai  binciken kwakwaf na manyan motoci.
Daga karshe ya yi fatar aikin bakin iyakar zai kammalu cikin lokaci ta yadda  za su  ci gaba da jin dadin gudanar  da aikinsu.