✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jam’iyyar PRP za ta yi waje da APC da PDP a zaben 2023 – Falalu Bello

Shugaban Jam’iyyar PRP ta Kasa, Malam Falalu Bello ya bayyana cewa jam’iyyar za yi bakin kokarinta wajen doke jam’iyyun APC da PDP a zaben shekarar…

Shugaban Jam’iyyar PRP ta Kasa, Malam Falalu Bello ya bayyana cewa jam’iyyar za yi bakin kokarinta wajen doke jam’iyyun APC da PDP a zaben shekarar 2023 mai zuwa.

Malam Falalu Bello ya ce sauran jam’iyyu ma ba za su samu galaba a kan Jam’iyar PRP ba domin PRP ta shirya tsaf wajen ganin ta taka gagarumar rawa a zabubbuka masu zuwa.

Malam Falalu Bello ya bayyana haka ne a wajen babban taron shugabannin jam’iyar na kasa da aka gudanar a Kaduna a ranar Asabar da ta gabata. “Zan so yin amfani da wannan dama in tabbatar wa ’yan uwana ’ya’yan Jam’iyyar PRP cewa an wuce  zamanin damuwa da rashin tabbas a jam’iyyar. Domin jam’iyyarmu ta PRP a shirye take yanzu domin tunkarar kalubalen da ke gabanta.

“Mu da muke cikin wannan jirgi da zai yi wuya a  tsayar da tafiyasa, akwai bukatar mu kara kaimi a tafiyar nan. Wadanda kuma ke waje har yanzu ya kamata tun wuri su shigo domin babu mai iya dakatar da mu a yanzu,” inji shi.

Malam Falalu Bello ya kuma ce an shirya taron ne domin a karbi sakamakon rahotannin kwamitocin da aka nada gab da zaben bara, domin duba matsaloli da kalubalen da ke fuskanta jam’iyyar a siyasar kasar nan da nufin yin gyara,” inji shi.

Kwamitocin sun mika sakamakon rahotanninsu lokacin taron ga shugabannin jam’iyyar.