Rahotanni na bayyana cewa, jirgin saman kamfanin Ethiopian Airlines Boeing 737 ya yi hadari a kan hanyarsa daga birnin Addis Ababa zuwa Nairobi babban birnin Kenya da fasinjoji 157.
Hadarin ya faru ne da misalin karfe 08:44 na safe agogon can a yau Lahadi, jim kadan bayan da ya tashi daga babban birnin kasar Ethiopia.
A wata sanarwa da kamfanin ya fitar ya ce za a fara aikin ceto, sai dai ya ce ba a san adadin mutanen da hadarin ya rutsa da su ba tukuna.