✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jonathan ya kai wa Buhari ziyarar godiya

Kammala aikin jirgin kasa ya nuna Buhari bai watsar da ayyukan gwamnatocin baya ba, inji Jonathan.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi wata ganawa da tsohon Shugaban Kasa Goodluck a ranar Talata 21 ga watan Yuli.

Jonathan wanda ziyarsa ta zo bayan a ranar Asabar Shugaba Buhari ya sanya sunansa, Goodluck Jonathan, a tashar jirgin kasa ta Agbor, ya yaba wa Buhari kan kammala ayyukan da gwamnatocin baya suka fara.

“Ina amfani da wannan dama wajen jinjina wa Shugaban Kasa a bainar jama’a, duk da cewa na aika masa da wasikar godiya.Abu mai kyau ne. Kazalika kammala aikin jirgin kasan ya tabbatar da cewa shugaban kasa ya ci gaba da ayyukan da gwamnatocin baya suka fara ba, wanda shi ne abin da ya kamata a rika ka yi”, inji shi.

Ya shaida wa ’yan jarida Fadar Shugaban Kasa cewa akwai kyakkyawar danganka a tsakaninsu kuma zai ci gaba da kawo masa ziyara.

Tashar jirgi ta Goodluck Jonathan da ke Agbor, ita ce mafi girma a layin jirgi da ya tashi daga Itakpe a jihar Kogi zuwa Sapele a Warri a Jihar Delta.