✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kamfanin suga na Hadejia zai fara aiki a shekarar 2015

Kamfanin suga na jahar Jigawa da ke Hadejia da aka gina tun zamanin  tsohon gwamnan jahar Alhaji jihar Jigawa Ibrahim Saminu Turaki  wanda iyalan marigayi…

Gwamna Sule Lamido na Jihar JigawaKamfanin suga na jahar Jigawa da ke Hadejia da aka gina tun zamanin  tsohon gwamnan jahar Alhaji jihar Jigawa Ibrahim Saminu Turaki  wanda iyalan marigayi Janar  Sani  Abacha  suka saya  zai fara aiki  a shekarar 2015.
Iyalan marigayin sun  ziyarci kamfanin kwanan nan inda suka bayyana cewa za a bude kamfanin ne da nufin samar wa matasa aikin yi a yankin  masarautar  Hadejia da kuma jahar  Jigawa baki daya.
Gwamnatin Sule Lamido ce ta sayar da kamfanin ga iyalan marigayi Sani Abacha kasancewar  ita gwamnatin jahar ba za ta iya cigaba da gudanar da kamfanin ba.  
Daraktan sahin kere-kere na kamfanin Malam Umar Sanda ne ya sanar da manema labarai haka a lokacin da suka ziyarci  kamfanin.
Malam Sanda ya kara da cewa, tunda iyalan marigayi Abacha suka mallaki kamfanin ba su ziyarce shi ba saboda abin da suka kira rubabbun injina da ke kamfanin, abin da ya zame wa iyalan marigayin dole su samar da injina masu inganchi don ganin kamfanin ya soma aiki gadan-gadan domin yin gogayya ga sauran takwarorinsa dake fadin kasar nan.
Ya kara da cewa, hukumar  kula da kogin Jama’are da Hadejia za ta bai wa kamfanin hekta 4000 da zai  dasa irin rake, kuma da zarar kamfanin ya fara aiki zai dauki ma’aikata 756 na wuccin-gadi a bangarori daban-daban na kamfanin.
Haka kuma zai dauki  mutane kamar 2,500 ‘yan asalin yankin masarautar  Hadejia aiki da kuma wadanda ba ‘yan jahar ba.