Gwamnatin jihar Legas ta sake sallamar karin mutum hudu da suka warke daga cutar Coronavirus a jihar.
A sanarwar da gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya fitar a shafinsa na twitter ya shaida cewa, mutum uku daga cikin mutanen da suka warke mata ne ragowar dayan namiji ne, ya ce dukkaninsu sun warke an kuma sallame su a yau Juma’a.
Ko a ranar Alhamis ma gwamnatin jihar ta bada sanarwar sallamar mutum 11 da suka warke daga cutar.
A ‘yan kwanakin nan ne Kwamishinan lafiya a jihar Legas Farfesa Akin Abayomi, ya bada tabbacin cewa majinyata cutar Coronavirus a Legas na murmurewa sosai kana babu alamar mutuwa a tare da su.