Karin ‘yan Najeriya da ke zaune a kasashen waje sun sake dawowa gida yayin da ake ci gaba da kokarin yakar cutar coronavirus a fadin duniya.
Rukunin ‘yan Najeriyan sun sauka na a filin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Asabar, inda aka tantance su.
At the Nnamdi Azikiwe International Airport, we were part of @Fmohnigeria delegation to receive Nigerian citizens on return
Our role is to provide passengers with public health guidance for their mandatory supervised quarantine to ensure saftey for themselves & all Nigerians pic.twitter.com/fnYnS3NFEw
— NCDC (@NCDCgov) May 23, 2020
Daga nan an killace su na tsawon kwanaki 14 domin tabbbatar da ba sa dauke da cutar coronavirus, kamar yadda doka ta tanada.
Jami’an hukumomin lafiya da suka haka da ma’aikatar lafiya ta tarayya da hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa da jami’an hukumar shige da fice ne suka tarbi mayan bakin.