✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Karkarin kokarin kofin kirkirar korafi

Baban-burin-huriyya A kara kaimin gyara A dakile masu waftar gara A gargadi masu kwado da dara A kyautata Haurobiya   Kuri’unmu an zube Kai musu…

Baban-burin-huriyya

A kara kaimin gyara

A dakile masu waftar gara

A gargadi masu kwado da dara

A kyautata Haurobiya

 

Kuri’unmu an zube

Kai musu kurin zobe

Ko a Jihar Yawon-bebe

Na gaida Makau da Asabe

Kui ta lumanar hana dambe

 

’Ya’yan danboto

Ku yasar da kwarmato

Saurayin-kirinki ya subuto

Hakkin talaka sai an kwato

Tuni na samu rahoto

 

Turka-turkar tumurmutse tunkuza

Magabta sun ga haza

Gwarzon gwaraza

Ga gwaza

Baba ya zame musu kazaza

 

Mui sammako

Mun samu sakamako

Mai mamako

Sai mu kandami koko

Ayyuka su baibaye kowane loko

 

Jam’iyyar tsintsiya

Kar ai tsiyatakun tsiwar tsiya-tsiya

Karnai na kada wutsiya

Haushinsu sunkutar mikiya

An dai sha kan makiya

 

An yi zabi-sonka

Saura rikon ragama

A daina duk wata rigima

Aikin gama ya gama

Kowa ya zo mui harka

 

Masu harkalla

Za a tsabga musu bulala

Sui ta lalala

A halin kila-wa-kala

Sai ma an raba salala

 

Al’umma ta sha wahala

Sai a sama mata walwala

Kowa-da-kowa a kula

Sai mu sakata mu wala

An kawar da masu gilla

 

Shirin sharbar shawarma

Sandar samun makama

Daga kasa zuwa sama

Kowa ya kara himma

A bibiyi bukatu masu kima

 

Kasa ta samu madogara

A daina kara-kara

Laluben damfara

A farga da kamun fara

Kowane kuskure a gyara

 

Harobiyawa nai kira

Al’umma ban da kangara

A hori masu fandara

Hukunci ba jira

Tsintsiya ai ta shara

 

A bude kasuwa

A sawo tantakwashin kasusuwa

Ban da dira wawa

Ko hatsaniya da kokowa

Mu ji dadin kai-kawo gari da dawa

 

Zaman lumana

Ya wanzu a ko’ina

In an hana cin amana

A tarairayi juna

Tare da tarin kauna

 

Kwakkwafi

Kokarin kofi

Karajin karfi

Kicifin kan karofi

Kutu-kutun korafi

 

Sakon-dussa

Sarkin-dusa

Sakamakon mai dasisa

Sare-sarin suburbuda tusa

Sarauniyar kisisinar kissa

 

Asibicin arangamar Arewatawa, Asabe da makau sun maka wa Baban-burin-huriyya marka-markar ruwan kuri’u, inda jam’iyyarsa mai alamar tsintsiya ta tattara ta yi musu kurin zobe, har a Jihar Yawon-bebe, inda Baba ya lula ya yi famfalakin raba ni da man-kaza, mai hankoron tafka TURKA-TURKAR TUMURMUTSE TUNKUZA. Hakika zababbakar zabukan shekara ta dubu karamin lauje da sili da manuniyar kasa ta kayatar, domin duk wanda ya yi yunkurin kwata tataburzar tabargazar WURU-WURUN-BEBE, tuni ya sha kashi a hannun BABE namijin fara.

Haurobiyawa wadanda zababbakar zabukan wannan shekara ta haifar musu takun-saka da juna, ya kamata a himmatu ka’in-da- na’in wajen tabbatar da wanzuwar zaman lumana a ko’ina, tare da tarairayar juna da tarin nuna kauna.

’Yan makaranta masu falle shafukan mujallu da makalu da baje na-zomo a akwakun batutuwa, lokaci ya yi da za a kara kwazo, amma a rage kwakwazo, wajen kiran kowa-da-kowa ya zo, mu bi zugar gwarzo, wajen hana ALARAMMAN ALMAJIRAN AREWATAWA bin dandazon cin kanzo. Don ta haka ne kawai za mu iya yi wa mazaje kozo. Lallai a kara kwazo. Kai na tuno aminina Yakubu Bazo-bazo.

Tuni dai an hana KUNDUGE KWANGEN KWAGE, don haka kowa ya dage, mu rabarbashi miyar dage-dage. Lallai batutuwa su kasance babu kage. Duk da haka wannan ba ta hana wasan ’yar burun-burun tsakanin bera da mage.

Zan karkare darasin makon nan, ta hanyar zaburar da Baban-burin-huriyya da Usainin-Babajo kan cewa babu hutu, sai ku jajirce wajen tunkarar dimbin kalubalen da ke addabar kasar nan, lallai a warware mana sasarin BANKE BOBO DA KWAMBON BOKOKO, don mu ji dadin kwankwadar KOKO. Hatsaniyar hautsinin Fullo da mai sana’ar na-duke, lamarin tuni ya kuke, kar a bari sarkakiya ta sassarke. A tsarin tsimi da tanadi, wajibi ne a hana TSUWURWURTA TSIMIN TSAMIYAR TA’ADAR TADA ADDAR TA’ADI, lamarin da ya haifar wa al’ummar kasar nan TSININ TSITAKAR GA LUKUDI, GA LAKUME KUDI; kai har ma KUSHEWAR KUDI aka bankado.

Wai na ji SAKON-DUSSA ja-gaban jam’iyya mai danboto da sanda jirge na ta hatsaniyar hargitsa al’umma, inda ya yi nuni da cewa wai TSARINSU NA DAMA-DAMAR-KURDA-KURDAR SIYASAR DAMO-DA-KURA-DA-DIYYA na fuskantar barazana, saboda kawai an yi kokowar kada kuri’u KANEN BABA-OJO ya sha kaye kasa warwas. Wai abin tambaya a nan shi ne, zamanin mulkin mulaka’u na mai danboto da sanda jirge, inda ta shafe shekaru sili da manuniyar sama tana yi wa DAMON-KURAR-DIYA karan tsaye, wane ne ya tuhume su, ko ya jefa musu azargagiyar zargin tafka ta’asa a kwanon tasa? Ko ma dai wacce irin amsa aka bayar game da tambayar da na bijiro da ita, ina jan na-zomon al’umma cewa, “ba ma bukatar Karkarin kokarin kofin kirkirar korafi.” Idan ma kun ki ji, to ba kwa ki gani ba.

Kafin mu fara SHIRIN SHARBAR SHAWARMA, wajibi ne mu daura damarar shawarwari nagari a wajen Baban-burin-huriyya, tare da rokon Mai-duka, Mai-kowa, Mai-komai Ya jibinci lamarinsa, ta yadda zai samu kuzarin kyautata ayyuka. Mu kuwa mu zamo al’ummar da ke karkashin jagorancin NAGARGARU, wadanda suka GYARU, za su MORU, kuma kada a bari kowa ya KWARU.