Sojojin Koriya ta kudu sun bayyana cewa Koriya Ta Arewa ta sake harba makami mai linzami mai cin gajeren zango a karo na biyu, kasa da mako daya a wani yunkuri na dawo da gwajinta na nukiliya.
Makamin da aka harba daga Arewa maso Yammacin birnin Kusong ya yi tafiyar kilomita 420 da 270 inda ya doshi Gabas.
Gwajin na zuwa ne sa’o’i bayan isar jami’an Amurka Koriya ta Kudu domin farfado da tattaunawa kan shirin kasar na makamin nukiliya.