✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta ba da umarnin kai El-Zakzaky gidan yari a Kaduna

Wata babbar kotu da ke  Kaduna ta yanke hukuncin mayar da jagoran kungiyar mabiya shi’a IMN Sheikh Ibraheem El-Zakzaky da matarsa gidan yari, bayan lauyoyinsa…

Wata babbar kotu da ke  Kaduna ta yanke hukuncin mayar da jagoran kungiyar mabiya shi’a IMN Sheikh Ibraheem El-Zakzaky da matarsa gidan yari, bayan lauyoyinsa sun ce an hana su izinin ganawa da shi daga hannun hukumar tsaro ta farin kaya DSS.

Kotun ta yanke hukunci ne a safiyar yau Alhamis, inda ta ce za a mayar da su gidan yarin ne don lauyoyinsu da likitocinsu su samu damar ganinsu cikin sauki.

Lauyan El-Zakzaky da matarsa Zeenatu, Femi Falana SAN wanda Barista Haruna Magashi ya wakilta ya ce an hana su gana da su ne tun bayan dawowarsu daga kasar Indiya.