Babbar kotun jihar Legas ta baiwa tsohon Gwamnan Jihar Abiya Orji Uzor Kalu wa’adin kwana bakwai don gabatar da kansa a gaban kotun.
Alkalin kotun Mohammed Idris ne ya sanar da hakan a jiya Litinin lokacin da ake sauraran karar da aka shigar a Legas.
Kotun dai na tuhumar tsohon Gwamnan da karkatar da kudin da ya kai naira biliyan 7.65.