Babbar Kotun jihar Kaduna ta bada belin shugaban Mabiya Kungiyar ‘yan Uwa Musulmi ta Shi’a (IMN) Shaikh Ibraheem Zakzaky domin ya samu damar tafiya kasar Indiya neman magani.
Shugaban IMN din na fama da rashin lafiya a sakamakon harbinsa da sojoji suka yi tun a shekarar 2015.
Kotun ta ce, shaikh Zakzaky da matarsa Zeenat na iya tafiya asibitin Mandeta da ke a Birnin New Delhi, Indiya domin a duba lafiyarsu.
Cikakken rahoton na nan tafe.