✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta hana ’yan kwadago shiga yajin aiki

Kotun ta ce kar kungiyoyin su shiga yajin aikin da suka yi niyyar farawa

Kotun sasanta rikicin ma’aikata ta dakatar da kungiyoyin kwadago da mukarrabanta shiga yajin aiki ko hana ma’aikata gudanar da ayyukansu daga ranar Litinin 28 ga Satumba.

Ta umarci kungiyoyin da jami’ansu, wakilansu ko wani duk wani mai hulda da su kar su kuskura su kawo tsaiko ga gudanar da ayyuka ko hana ma’aika da sauran ’yan Najeriya gudanar da harkokinsu a ranar ko wata rana ta daban.

Mai Shari’a Ibrahim Galadima ya ce hakan al’amura za su ci gaba da kasancewa har sai kotun ta yi saurari karar da aka shigar a gabanta.

Wata gamayyar kungiyoyin wanzar da zaman lafiya ce ta shigar da karar tana neman kotun ta hana kungiyoyin kwadago shiga yajin aiki.

Idan ba a manta ba kungiyoyin kwadago sun yi barazanar fara yajin aiki da zanga-zanga a fadin Najeriya domin matsa wa Gwamantin Tarayya lamba ta soke karin farashin man fetur da wutar lantarki da aka yi.