✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta kori Sanata Dino Melaye ta bayar da umarnin sake zaben

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta kori Sanata mai Wakiltar Kogi ta Yamma Dino Melaye, a jihar Kogi. Kotun ta yanke hukuncin hakan ne…

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta kori Sanata mai Wakiltar Kogi ta Yamma Dino Melaye, a jihar Kogi. Kotun ta yanke hukuncin hakan ne bayan sauraron kararrakin zaben ‘yan majalisar tarayya da na jihohi da aka shigar.

Kotun ta ce, ba a gudanar da sahihin zabe ba wajen zabar Sanata Dino Melaye, wanda ke takara na jam’iyyar PDP.

Kotun ta umarci Hukumar zabe ta kasa INEC da a sake gudanar da zaben mukamin Sanata Dino daga yanzu zuwa kwanaki 90.