Bayan Kotun sauraron kararrakin zabe a Najeriya ta yi watsi da karar da tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku Abubakar, wanda ya shigar a gabanta, inda yake kalubalantar zaben Shugaba Muhammadu Buhari da aka yi zaben watan Fabrairun 2019.
Kotun karkashin jagorancin Mai Shari’a Muhammad Garba ta tabbatar da Shugaba Buhari na jam’iyyar APC mai mulkin kasar a matsayin halastaccen wanda ya lashe zaben takarar Shugaban Najeriya.