✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Majalisar Amurka na ci gaba da binciken tsige Trump

Majalisar Dokokin Amurka ta saurari shaidu da yawa a binciken yuwuwar tsige shugaban Amurka Donald Trump a bainar jama’a. WASHINGTON DC – An fara sauraren…

Majalisar Dokokin Amurka ta saurari shaidu da yawa a binciken yuwuwar tsige shugaban Amurka Donald Trump a bainar jama’a.

WASHINGTON DC –

An fara sauraren ne da safiyar Talata tare da shaidu uku da kuma abin da suka sani akan zargin da ake yiwa Shugaba Trump na yunkurin tursasawa Ukraine ta binciki abokan hamayyarsa.

Duka dai, kwamitocin Majalsir Wakilan sun saurari shaidu tara ne a lokacin zama biyar daban daban da aka yi ranakun Talata da Laraba da kuma Alhamis na wannan makon.

Sai dai shaidar da aka fi saka ido ta zone daga jakadan Amurka a kasashen Tarayyar Turai da ya bada gudummuwar dala miliyan daya ga kwamitin shirye shiryen rantsar da shugaba Trump, Gordon Sondland.

Da alama Sondland ya taka rawar gani a tattaunawar tare da Ukraine akan zargin da ake yi cewa Shugaba Trump ya bukaci Ukraine ta binciki wanda ake ganin zai kalubalance shi a zaben Shugaban kasa na 2020, kuma tsohon mataimakin Shugaban Amurka, Joe Biden, akan cin hanci.