✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Manjo Hamza Almustafa: Ba na shakkar daukaka karar da Jihar Legas ta yi

Manjo Hamza Almustafa,  wanda   ya yi  kwanaki  39  da fitowa daga gidan kurkuku, bayan ya kwashe shekaru 15 a tsare bisa zarginsa da aikata laifuffuka…

Manjo Hamza Almustafa,  wanda   ya yi  kwanaki  39  da fitowa daga gidan kurkuku, bayan ya kwashe shekaru 15 a tsare bisa zarginsa da aikata laifuffuka 4,  ciki har da  kashe matar marigayi Cif Abiola, aka yanke masa hukuncin kisa a ranar 30 ga watan Janairun shekarar 2011, ya yi tsokaci kan daukaka karar da Jihar Legas ta yi.
Bayan yanke wannan hukunci ne, sai  ya daukaka  kara, inda wasu alkalai 3 karkashin Mai shari’a Amina Augie suka yi watsi da karar. Bayan hukuncin ne sai gwamnatin Jihar Legas ta daukaka kara tare da hujjoji 14  da ta ke jin bai dace a ce an sallami mutanen biyu ba.
Yayin da wakilin Aminiya ya tuntubi Manjo Almustafa kan haka, sai ya ce ko jikinsa, domin tun farko karya ce ta daure su kuma gaskiya ta sake su don haka ko sau nawa gwamnatin za ta daukaka  kara  wannan ba  abin damuwa  ba ne a gare shi.
Ya ce gwamnatin jihar ta Legas, tana da ’yancin daukaka kara  domin ba wani abu ne ta yi sabo ko kuma wanda ya saba wa  dokar kasa ba, lamarin da shi ma tuni ya sanar da lauyoyinsa  domin sanin matakin da za su dauka game da wannan yunkurin.
Manjo Almustafa ya ce wannan ba zai rage shida kome ba  domin kuwa a halin yanzu shi mutum ne mai cikakken ’yanci kuma zai ci gaba da walwala kuma wannan daukaka  karar  zai kara  tono wasu abubuwan da  a da ’yan Najeriya  ba su san da su ba. Ya yi kira  ga masoyansa  da kar wannan lamari ya  razana su.