Mazauna Osogbo, babban birnin jihar Osun sun daka wawa a wani rumbun ajiye kayan abinci da Gwamnatin Tarayya ta ba jihar a matsayin tallafin COVID-19.
A ranar Juma’a dandazon jama’a sun yi wa ma’ajiyar da ke kamfanin CPI a Ede tsinke tare da kwashe kayan abinci daga cikinta.
- Yadda masu zanga-zanga suka sace kayan abinci
- Zanga-zangar #EndSARS ta jawo asarar biliyan 400 a Legas
- Kasashe sun bamu Dala 400,000 – Masu zanga-zangar #EndSARS
An hangi mutanen na ta jidar kayan da suka hada da shinkafa, taliya da dai sauransu ba tare da shamaki ba.
Sai dai yunkurin jin ta bakin gwamnatin jihar kan lamarin ya ci tura sakamakon kin daukar wayarmu.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoton mutane na ci gaba da yin tururuwa sun dibar kayan.
A halin da ake ciki zanga-zangar #EndSARS na ci gaba da gudana a sananniyar unguwar nan ta Olaiya da ke birnin na Osogbo.
Gwamnatin jihar dai ta janye dokar hana fita ta sa’o’i 24 da ta sanya a a ranar Laraba.