✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mataimakin Shugaban Kasar Gambiya ya rasu a Indiya

Shugaba Adama Barrow ne ya sanar da rasuwar a shafinsa na Twitter

Mataimakin Shugaban Kasar Gambiya, Badara Joof, ya rasu a kasar Indiya.

Shugaban Kasar, Adama Barrow ne ya sanar da rasuwar a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter da safiyar Laraba.

“Ya ku ’yan uwana ’yan Gambiya, cikin yanayin jimami da alhini nake sanar muku da rasuwar Mataimakina, Mai Girma Badara Alieu Joof. Ya rasu ne a kasar Indiya bayan wata gajeruwar rashin lafiya. Allah Ya jikansa Ya ba shi aljannar Firdausi,” kamar yadda Adama Barrow ya wallafa a Twitter.

To sai dai sanarwar ba ta bayyana lokacin da ya rasu ba, da kuma ko ya je ganin likita ne kafin rasuwar tasa.

Badara Joof dai ya yi karatunsa a Jami’ar Bristol da kuma digirinsa na biyu a fannin Adabin Turanci daga Jami’ar Landan da kuma a fannin Tattalin Arziki daga Jami’ar Bath.

Ya fara aikin gwamnati ne a matsayin malamin Turanci a Kwalejin Gambiya.

A shekarar 2014, Bankin Duniya ya nada Badara a matsayin kwararren jami’in ilimi a kasar Senegal.

A ranar 22 ga watan Fabrairun 2017, Shugaba Adama Barrow ya nada marigayin a matsayin Ministan Ilimi mai Zurfi, Bincike da Kimiyya da Fasaha.