✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Matasa dubu 14 za su gudanar da aikin zabe a Jigawa

Ma’aikatan wucin-gadi dubu 13 da 970 Hukumar Zabe ta Kasa (INEC)  a Jihar Jigawa ta dauka aikin zaben da za a fara gudanarwa a gobe…

Ma’aikatan wucin-gadi dubu 13 da 970 Hukumar Zabe ta Kasa (INEC)  a Jihar Jigawa ta dauka aikin zaben da za a fara gudanarwa a gobe Asabar.

Shugaban Hukumar INEC a Jihar  Dokta Mahmud Isah ya tabbatar da haka a wani taron manema labarai da hukumar ta kira a shekaranjiya Laraba a ofishinsa.

Ya ce kimanin mutum dubu 60 ne suka nemi aikin zaben amma gaba dayan wadanda hukumar ta dauka ba su kai mutane dubu ashirin ba.

Ya musanta jita-jitar da ake bazawa, cewa wadansu daga cikin ma’aikatan hukumar ne suka yi kama-karya wajen ba da sunayen wadanda za su yi aikin zaben. Ya ce hakan ba gaskiya ba ne.

Ya kara da cewa sun tanadi ma’aikatan tsaro a daukacin kananan hukumomin jihar da za su bai wa ma’aikatan zaben da kayan zaben kariya kafin da kuma lokacin zaben da kuma bayan an kammala.