✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Matsalar talauci da rashin aikin yi a Najeriya: Laifin gwamnati ko na al’umma?2

Dukkan alkaluman da ake amfani da su na tantance bunkasar tattalin arzikin kasa sun nuna yadda talauci da rashin aikin yi suka yi katutu a…

Dukkan alkaluman da ake amfani da su na tantance bunkasar tattalin arzikin kasa sun nuna yadda talauci da rashin aikin yi suka yi katutu a Najeriya. Abin tambaya a nan shi ne, shin wa za a dora wa alhakin kasancewar haka, gwamnati ko al’ummar kasa? Ga ra’ayoyin jama’a, kamar yadda wakilanmu suka kalato mana:

Gwamnati ce da laifi – Ibrahim Ahmadu

Ibrahim Ahmadu: “Wato gaskiyar lamarin, gwamnatin Najeriya ita ce da babban laifi a kan batun talauci da yake ci gaba da addabar al’ummar kasar nan dalili kuwa shi ne, ita ce take da wuka da nama amma sai ya kasance shugabanni a karkashinta suka bi suka kashe kasa baki daya, babu tsaro da zai ba kasashen waje amincewar zuba jari a kasar nan. Tattalin arzikinmu ya ruguje, babu kamfanoni ko wasu masana’antu masu yin aiki kai tsaye ballantana a samu aikin yi, sannan kuma idan aka lura sosai da idon basira, sai a ga cewa gaba dayan shirin gwamnatin ya kare ne cikin yaudara da rudani, domin gwamnatin ba ta ba al’ummar kasar nan damar sanin inda ta sa gabanta.”