✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Muna so gwamnati ta matsa kaimi wajen hana shigo da makamai’

Matasa   Mazauna  Jihar  Legas  sun koka kan yadda  shigo da makamai ya zama ruwan  dare  a Najeriya, abin da yake haddasa aikata ayyukan taddaci a…

Matasa   Mazauna  Jihar  Legas  sun koka kan yadda  shigo da makamai ya zama ruwan  dare  a Najeriya, abin da yake haddasa aikata ayyukan taddaci a kasar baki daya, saboda haka suka bukaci gwamnati ta matsa kaimi wajen daukar kwakkwaran mataki na dakile shi.
Matasan da suka kira kansu kungiyar matasa  masu neman  wa matasa  aikin yi a cikin kasa,  sun yi wannan kiran ne a wajen taron manema   labarai  da suka kira inda suka bayyana cewa a   binciken  da suka gudanar,  sun gano  cewa  ana  yawan  shigo da  makaman  ne ta ruwa  domin bakin  iyakokin  Najeriya  ta  ruwa  ba su da  wadataccen  tsaron da ya kamata.
Shugaban kungiyar, Comrade Umar Isma’il  ya ce  shigowa  da makamai  barkatai  kuma  da  rashin tsaron da  bakin iyakokin Najeriya  ta ruwa ke  fuskanta  ya sa  da yawan  matasan  da  suka samu  damar  mu’amala da  wadannan makamai  suke aukawa  cikin  aikin  ta’addanci.
Comrade Umar ya ce kungiyarsu tana bayar da  shawarar gwamnati  ta samar  da  sojoji ruwa da ake kira da Turanci ‘Merchant Naby’ kwatankwacin wadanda  ake da su a kasar  Kanada da  Amurka da Ingila da wasu kasashen da suka ci gaba.
Comrade Umar ya ce yana da jin kwarin gwiwar  cewa  muddin  aka  samar  da  wadannan  sojoji za a samar da raguwar  shigowa  da makamai  cikin Najeriya ko ma a dakile lamarin baki daya,  kana kuma ya samar  da aikin yi ga matasa  ko kuma al’ummar kasa, domin idan za a dauki wadanda  za su yi wannan aikin, matasa  su ne suka fi dacewa su yi shi.
Shi ma daya daga  cikin  shugabannin kungiyar,  Comarade Ya’u Basula Zuru da yake  tofa albarkacin bakinsa game da samar  da  wadannan sojojin,  ya nuna ba kasashen da  suka ci gaba kadai suke da su ba, hatta  a wasu kasashen Afirka  irin Afirka ta Kudu da Ghana suna da su, lamarin da ya sa suke samun rashin kwararar makamai a cikin kasashensu.
Ita ma Mis Maggi Kateiko,  daya daga  cikin shugabannin kungiyar,  ta yi  karin bayani kana wadancan sojoji na ruwa da cewa ba su da bambanci da kifi domin  sukan kwashe kwanaki cikin ruwa domin gudanar da aikin ko-ta-kwana.
Ita kuwa Hajiya Fatima Altine, a tata shawarar cewa ta yi  samar da sojojin ruwan zai kara wa masu saka hannun jari kwarin gwiwar shigowa Najeriya. “Muddin harkokin tsaro  suka  inganta,  to  da yawan ’yan kasashen waje za su yi ribibin shigowa cikin kasar nan domin samar da masana’antu,  wanda  hakan yana nufin karin samar da aikin yi ke nan, musamman ga matasa”, inji ta.