✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAHCON ta soma jigilar Alhazai zuwa gida Najeriya yau

Hukumar Jindadin Alhazan Najeriya ta Kasa  (NAHCON) a yau Asabar ta soma jigilar Alhazai zuwa gida Najeriya bayan kammala aiki hajin bana. Hukumar tun farko…

Hukumar Jindadin Alhazan Najeriya ta Kasa  (NAHCON) a yau Asabar ta soma jigilar Alhazai zuwa gida Najeriya bayan kammala aiki hajin bana.

Hukumar tun farko ta sanar da yau a matsayin ranar fara jigilar Alhazai zuwa gida Najeriya.

An soma yin jigilar ne da alhazan jihar Legas su 432 a jirgin‎ Flynas mai lamba XY7434 wanda ya taso daga filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da ke Jeddah.

A cewar sanarwa daga sashen kula da jigila na Hukumar NAHCON, jirgin ya baro kasar Saudiya ne zuwa Najeriya da misalin karfe 3 na kasar watau karfe 1 kenan a Najeriya.

Kuma ana sa ran isowar Alhazan gida Najeriya watau na jihar Legas da misalin karfe 6 na yammancin yau.