Gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana fargabarsa akan cewa, Najeriya za ta iya fadawa cikin matsin tattalin arziki idan ba a dauki matakan magance yawan rashin ayyukan yi ba a Najeriya da wasu matsaloli da ake fuskanta a fannin tattalin arziki.
Gwamnan CBN Godwin Emefiele, ya bayyana hakan ne a yau yayin gabatar da jawabi a mai taken ‘matsalolin da suka dabaibaye harkar kudade a duniya’ wanda aka yi a jami’ar Benin.