✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NUC ta umarci jami’o’i su fara shirin budewa

Hukumar Kula da Jami'o'i ta umarce su da su fara shirye-shirye nan take

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Najeriya (NUC) ta umarci dukkannin jami’o’i da su fara shirye-shirye nan take domin ci gaba da karatu baya rufe sakamakon bullar cutar COVID-19.

Sanarwar da NUC ta aike wa Shugabannin Jami’o’i ta ce hakan na zuwa ne duba da raguwar masu cutar da bullarta ta sa aka rufe makarantun a a ranar 23 ga watan Maris, 2020.

“Sakamakon jawabin Kwamitin Shugaban Kasa kan Yaki da COVID-19 cewa an samu raguwar masu cutar sosai, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta amince da bukatar NUC na cewa jami’o’i su fara shirye-shirye nan take domin ci gaba da harkokin karatu”, inji sanarar.

Ka’idojin bude jami’o’i

Sai dai hukumar ta gindaya sharudda biyar da ya wajaba kowace jami’a ta cika kafin a bude ta domin gaba da karatu.

  1. Dole a kiyaye matakan kariyar da tsare-tsaren Hukumar Yaki da Cutttuka Masu Yaduwa ta Kasa (NCDC) na hana yaduwar cutar.
  2. Babu dalilin da zai sa a rusa tsarin zangon karatun NUC da ya danganci adadin kwanakin kowane zangon karatu.
  3. Dole ne a tabbatar da kiyaye dukkannin dokoki da ka’idojin NUC na tabbatar da inganci.
  4. NUC da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya za su kai ziyarar gani da ido domin tantance irin tsare-tsaren kare lafiya da ingancinsu a jami’o’i ta bangaren kayan aiki, dakunan karatu, ofisoshi, ajujuwa, dakunan kwanan dalibai, dakunan gwaje-gwaje, cibiyoyin kula da lafiya da sauransu.
  5. Dole ne daga lokaci zuwa lokaci jami’o’in za su rika sanar da NUC game da halin da suke ciki.