✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ranar Talata za a dawo Gasar Zakarun Turai

A ranar Talata mai zuwa ce za a dawo Gasar Zakaun Turai da aka kwana biyu ana hutu tun kammala zagayen farko na gasar. A ranar…

A ranar Talata mai zuwa ce za a dawo Gasar Zakaun Turai da aka kwana biyu ana hutu tun kammala zagayen farko na gasar.

A ranar Talata 18 da watan Fabrairu za a fara fafata wasannin farko na zagaye na biyu na gasar.

Kungiyar da ke rike da kambin, Liberpool za ta bakunci kungiyar Atletico Madrid a birnin Madrid, don fafatawa.

Liberpool tana tashe a yanzu haka, ita kuma Atletico Madrid tana fama da kwan-gaba-kwan baya a wasa a bana.

Ana sanya Liberpoop  a cikin kungiyoyin da za su iya lashe gasar, duk da cewa ita ce ta lashe gasar a bara.

Masu sharhi kan wasan kwallon kafa suna ganin tun lokacin da Liberpool ta lashe Gasar Zakarun Turai a bara,  likafar kungiyar yake ta kara gaba.

A daya wasan kuma a ranar  Talata, PSG ce za ta goge-raini da kungiyar Dortmund a Jamus.

Dukkan kungiyoyin akwai alamar a shirye suke, lura da yadda suke kokari a gasar gida da suke bugawa.

Sai kuma ranar Laraba, inda za a fafata atsakanin Atalanta da Balencia, sai kuma Tottenham ta fafata da kungiyar Leipzig a gidan Tottenham din.

Kasancewar Jose Mourinho ya karbi ragamar horar da Tottenham, wadansu na ganin kungiyar za ta iya bada mamaki a Gasar Zakarun Turai duk da cewa kungiyar na kwan-gaba-kwan-baya tun bayan da ya karbi ragamar daga tsohon kocin kulob din.