✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rudanin raurawar rabon rawunna (1)

  Mai martaba Masanin Sisi-da-sisi Hukumar Zakka da hubusi Raba masarauta ake bin bahasi Lalitarka aka ce ba ko asi Lamarin na da jefa wasi-wasi…

 

Mai martaba Masanin Sisi-da-sisi

Hukumar Zakka da hubusi

Raba masarauta ake bin bahasi

Lalitarka aka ce ba ko asi

Lamarin na da jefa wasi-wasi

 

Wassafa laifuka a tafi

A kai ta laluben laifi

Kai ka ba da kafa marar rufi

Aka wangale maka shafi-shafi

Har da bin kwakkwafi

 

Mun dai ga Majigin makafi

Bugun Shago a kai wa Maikarfi

Wai tagwaye sun yi kofi

Ka da dai a fada rafi

Masunta sun ce ruwan da zurfi

 

Babban mutum yai jaye-jaye

Rikon igiya na neman yai kaye

Akai ta yaye-yaye

A hankalta ’ya’ya da iyaye

Yau fa gari ya waye

 

Kai ne wane

Ko dan wane ne

Idan ka shiga bone

Ba ruwan kowa balle ai aune

Ka tsaya tsaf ka gane

 

Rudanin raurawar rabon rawunna

Rabe-raben kahonni tamfar raguna

Karaga ce da ka zauna

Daga bara zuwa bana

Kai ta taratsin magana

 

Fadin kasa

Aka karkasa

Mutane na ta busa

Wasu sun karke da sa-in-sa

Ka-ce-na-ce da kulla dasisa

 

’Yan kore na kalaman kafa kusa

Jagaliya ce ta siyasa

Doka ta malkwasa

Laifuka aka fallasa

Kasurar rigima wasa-wasa

 

Masu rawunna kadahan-kadaran

Ban da katsalandan

A bari sai an je Lantsandan

A haifar da matsaloli daban-daban

Rawa kan sauya da juyin wani kidan

 

Sai a rungumin juyin zamani

A bi tarbiyyar iyaye da kakanni

A rinka aiki da sani

A yasar da karambani

A bar yi wa juna gani-gani

 

Aiki da hankali

Amawalin Malam Mawali

Kasar da babu haraji da jagali

Ba a daukar kudi ai shagali

A bar takaddamar zare kansakali

 

Hawan dare sirdin akawali

Tufafi na ta kyalkyali

Kayan ado na walwali

Fadin kasa an yi fasali

A dai yi ginin kakkarfan tubali

 

Sunkurun siyasa na tafarfasa

Kisisinar kissa

Fafatawar samun fursa

In bodari zai karkare tusa

Kowa sai ya gurgusa

 

Birnin Dabo ba a dabo

Magabta sun lababo

Kulla-kullarsu a hanci na habo

Sun yi wa mahukunta tabo

Don neman sisi da kwabo

 

Masarautar Kare-kare

’Yan gari ne ba bare

Ko bakon Ba’are

Sai a kiyayi sare-sare

Komai an karkare

 

Rawanin-nono

Kawanyar bonono

Ana ta kwankwadar fura da nono

Ayyuka tuni an auno

Garma aka ce allura ta tono

 

Kasar Gayya-gayya

Su ma sun daura aniyya

Bayan tambura an yi jiniya

Inya-inya

Kamar kukan jinjiniya

 

Birnin Bin-cici

Dan marigayi mai adalci

Nadi akwai wa dan mutunci

Rike sandar yi wa jama’a sassauci

Kar a bari kowa ya shiga kunci

 

Mahukunta ai ta hukunci

Talakawa ka da ai butulci

A yasar da tumasanci

Don yawansa na sa kaskanci

Masu mulki a kiyayi zalunci

 

Kaftun kofaton kotu

Kararaki ne rututu

Baje batutuwan bututu

Koken masarautu

A daddale karatun rubutu

 

Indiyawan Maharaja

Raurawar rangajin Raja

Juyin akalar ragamar ja-in-ja

Tungar dagar mulki an ja

Batutuwa ne baja-baja

 

A Rasha an yi Sarki Za

Zamaninsa shi ak karzaza

Yai shuhurar kazaza

Mazaje sun yi bugun kiraza

Ahalinsa sun shude ga banza

 

Birtaniyawa

Har yau suna tattakawa

Sarauniyarsu na da kawa

Lamarinta da ban shawa

Ta rike al’umarta kowa-da-kowa

 

Can tsakiyar Gabashi kuwa

Larurar lamuran Larabawa

Sarakunansu na tagazawa

Adawar siyasa na angazawa

Damon-kurdiyya na dada kutsawa

 

Mun dai ga daba

A dambarwar gada-gadar Abba

Yamutsin  gundumin gudumar gaba

A hankalta ’ya’yan Inna da Baba

Kowa sai ya duba

 

***************

Doron damon-kurar-diya

Doron damon kurardiyar kurdiya karon farko da Gwamnatin Baban-burin-huriyya ta bullo da shi a watan Yawon-nunin-wuni, sabon biki ne a jerin ranakun bukukuwan Haurobiyawa, tun bayan dawowa tafarkin Dama-damar-kurda-kurdar siyasar damon-kurar-diya a shekara ta alif sili da muuniyar kasa da ta kasa da ta kasa. An kuma yi wannan namijin kokari ne don tunawa da birkitattar siyasar Haurobiya da ta yamutse zamanin mulkin Baraden bindiga, inda Malam Abiyo-Bala ya lamushe zabi-sonka aka soke, har ta gai ga ba a rantsar da shi a matsayin Shugaban Kasar Haurobiya ba, illa ma dai dauri da ya sha, har rai ya yi halinsa.

Fatanmu dai, wannan lamari ya kasance masalaha ce ga al’ummar kasar nan, sannan yadda ake ganin wadansu sun kwashi garabasar damon-kurar-diya, lallai akwai bukatar kowane yanki na kasar nan a dan jinko musu nasu kason. Bisa wannan dalili ne, nake ganin akwai bukatar ALARAMMAN ALMAJIRAN AREWATAWA da ’ya’yansa kolo da titiribiri da gardin garada a jinko musu nasu ROMON RAGON ROMAWA, ta yadda za su tsahirta da gararamba a kan tituna suna DANDAZON LALUBEN DAN KANZO, da zarar an aiwatar da wannan tsari, har ta kai ga wadannan rukuni na jama’a, sun tsinci kurungunsa a farfajiyar MAKEKIYAR MAKARANTAR MAMA ko a BABBAR BUKKAR BABAN-BURIN-HURIYYA, sai mu ce lallai sun kwashi romon ragon Romawan damon-kurar-diyya.

Kodayake dai ga manyan mutane masu rawunna da kambin gadon rikon ragamar jama’a da ke fama da kwaramniyar Gwamna gwarangwam, musamman a birnin Dabo, inda ba a dabo, Jihar Tumbin-giwa da Jihar Filfilon-toto, inda aka falle fila-filan bangon bangazar buga-bugar bugun bareman bare da nufin a ware. Shin ko su ma dai difara wa al’ummarsu aka yi romon ragon Romawa rurrumarawar rangajin ragargazar damo-da-kura-da-diya. Fatanmu dai ka da a daidaita al’umma. Sai dai mun jiwo cewa can a birnin Shehu Mujadaddi, Gwamna gwarangwam Tumbin-walawalar walle-wallen wulwulawar wulli na yunkurin karin la’adar kadagon kwadagon manyan mutane masu rawunna. Ta yiwu suma sun sharandabi shawarmar siyasa.

Haurobiyawa a sha ruguntsimin biki Fararat far-far a titi firirit!