✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rudanin raurawar rabon rawunna (2)

Tartsatsin taratsin tinkahon tereren tsokale-tsokalen takadamar sasarin samemen sa-in-sar Mai Martaba Masanin Sisi-da-sisi da Gwamna gwarangwam Gundumin gudumar gandun gangamin aikin artabun arangamar aika-aika da…

Tartsatsin taratsin tinkahon tereren tsokale-tsokalen takadamar sasarin samemen sa-in-sar Mai Martaba Masanin Sisi-da-sisi da Gwamna gwarangwam Gundumin gudumar gandun gangamin aikin artabun arangamar aika-aika da ta haifar da karkasa fadin kasar da a da ikon Babban mutum mai rawani na birnin Dabo ne, inda aka yi kashi tsayuwa bisa kafa guda, baya ga da’irar kawanyar birni, wato: Masarautar Kare-kare da Gayya-gayya da Birnin Bin-cici da Rawanin-nono.

Daukacin wadannan daulolin mulki da aka fitar, an shata su ne daga ainihin fadin kasar babban mutum mai rawani na birnin Dabo, wato Mai martaba Masanin Sisi-da-sisi, wanda ya bayar da kafa ga ’yan siyasa suka goga masa rabu, har ta kai ga sun yi masa fallasa, wai asusunsa BABU KO ASI. Ni dai na fasko cewa mafi yawan laifuffukan shaci-fadi ne, illa dai kawai Babban mutum mai rawani na binin Dabo ba ya son tu’ammali da amawali, sai ma fifita takadamar fito-na-fito da zare kansakali, har ma ya ja daga yayin da ya dare sirdin akawali.

Su kuwa ’yan siyasa, musamman Gwamna gwarangwam Gundumin gudumar gandun gangamin Aikin artabun arangamar aika-aika sai ya afka masa ta cikin ruwan sanyi, tamkar a yi, ba a yi ba. Haurobiyawa kun ga illar surutu rututu. Kai wannan dalilin ne ma ya sanya duk in na zo yin darasin makarantar nan sai na yi takatsantsan, don gudun kada in shiga gaban kamfanin Dillancin Labarai na Reuters, wai ni a yi ta jina ratatata!

Haurobiyawa, lokacin da Turawan Mulkin mulaka’u suka karbe ragamar mulki daga hannun masu rawunna, sai suka sake mika ragamar ta bayan fage, inda daga bisani suka yi wa al’umma sakiyar -da-ba-ruwa. Bayan da suka karkare wa’adin jan ragamarsu, sai suka damka kasar a hannun wadanda suka yi fafutikar ja-in-jar jan ragama a tafarkin damon-kurar-diya. Shi ke nan, an yi wa kasar nan wa-ka-ci-ka-tashi. Domin ko mun ki, ko mun so, har yanzu manyan mutane masu rawunna su ke tare da jama’a, suka san tsilli-tsillin matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya.

Shi dai Gundumin gudumar gandun gangamin Aikin artabun arangamar aika-aika ya shiga takun saka ne da Mai martaba Masanin sisi-da-sisi bisa zargin cewa, ya tattara cincinkarfinsa a gada-gadar Abbatin jar tagiyar kwankwatsa tsiyataku. Don haka duk da cewa an yi musu sulhu, inda Dangatan Kasuwa, tare da ’ya’yan kungiyar gangamin gwamna gwarangwam, sai ya yi turjiya, tare da kafiya babu yafiya, ya kuma fake da binciken badakalar wadaka da damin makudan matsabban masarauta.

Dadin wannan lamari dai, shi ne, irin tuhumar da Gundumin gudumar gangamin Aikin artabun arangamar aika-aika ke tuhumar Mai martaba masanin sisi-da-sisi, shi ma ya hau kansa, tunda ai JARUMIN JAYE-JAYEN JIFAR JAFA’IN JARIDAR DALILIN NAJERANGIYA ya bankado na babban mutum mai rawani na birnin Dabo; sannan daga bisani ya saki dodannin hotuna masu wuntsila gudi-gudi na gwamna gwarangwam yana soke damin matsabban Dalar dilar dalar Amurkawa. Bisa wannan dalili ina ganin gara a shafa wa wannan wuta da ke ruruwa ruwa kafin ta lakume al’umma, musamman ma ganin yadda talakawa ke biye musu. Kun ga ke nan babu tantama BUSHIYA CE KE SON YI WA KUNKURU KAFA ko?

Kuma daukacin Kaftun kofatun kotu, wato kararaki rututu da baje batutuwan bututu na jin koken masu nadin masarautu da ke hankoron ganin an daddale karatun rubutu, to an yi watsi da su. To ina mafita?

Lallai akwai bukatar mu fasko yadda ta wanye da manyan daulolin mulki a fadin duniya kamar Indiyawan Maharaja masu raurawar rangajin Raja, wadanda suka ga Juyin akalar ragamar ja-in-ja, inda tungar dagar mulki an ja, tare da batutuwa baja-baja.

Sai batun Rasha na wancakalar da Sarki Za, wanda a zamaninsa shi ne karzaza, wanda ya yi shuhurar kazaza, har mazaje suka yi masa bugun kiraza, har ahalinsa sun shude ga banza. Amma dai  Birtaniyawa, har yau suna tattakawa ga Sarauniyarsu na da kawa, domin lamarinta da ban-shawa, kuma ta rike al’ummarta kowa-da-kowa

Can tsakiyar Gabashi kuwa, akwai larurar lamuran Larabawa, inda sarakunansu ke tagazawa sai dai adawar siyasa na angazawa, domin Damon-kurdiyya na dada kutsawa.

Malam Sa’adunmu Na-Zungur, wanda ya nusar da mu yin zungur kada mu yi zugum, ya taba rera wakensa Arewa Mulukiyya ko Jamhuriyya?

Yau dai mun shiga JAMHURUN JAMHURIYYA tsundum, inda su Baban-burin-huriyya ke  ta tataburzar turka-turkar tunkarar Samarin-kusu da ’Yan matan jaba da gafiya da suka yi wa lalitar kasa karkaf, suka wawushe komai kakaf.

Batu na ingarman karfen karafunan tarragon titin kwangirin dogo, ba tare da bata lokacin wulkitawar tsinkayen tsinin hanayen agogo ba, rabe-raben rawunnan ragamar raba rigimar al’umma a birnin Dabo ci gaba ne, amma inda aka samu tasgaron tuma-da-gayya, shi ne, batun daukar fansa, wato fada ne ake fafatawa, wai DAN HALAK KA FASA; hasali ma wadansu so suke a farfasa, a fasa kowa ya rasa.

’Yan makaranta, masu falle shafukan mujallu da makalu da jaridu da wagagen littattafai, musamman masana kundayen labaran da, da na yanzu, lallai mu yunkura wajen ganin mun daidaita gargajiya a bisa turbar takun tafiyar zamani, ta yadda za a shawo kan taho-mu-gama kwatankwacin lamarin da ya wakana a birnin Dabo. Lallai a yi dokar kara wa masu rawunna karfin iko, ta yadda za su samu damar yi wa al’umma abin da ya dace, sannan a kafa kakarfar hukumar da za ta ja musu na-zomo da zarar sun baude.

Kin aiwatar da wannan dabara za ta sanya mu wayi gari a ce da mu sun shude, har ma an turbude, magabtanmu kuwa su yi mana zunde da gande-ganden rade-radin kulla makirci, shi ke nan, mun yi wasararairai, har an karke da asarar kyawawan ta’adun iyaye da kakanni.

Wani hanzari dai ba rarewa aguje ba, ya kamata mu fasko cewa, a tsukun Turai akwai masu rike da kambin sarautun gargajiya; sannan a nahiyar Asiya wasu sun shude, wasu kuwa suna ci gaba da aza sanwa. Kodayake Indiyawa sun kaskantar da sarautun Raja da Maharaja, tunda yanzu ba su da wani tasirin jan ragamar juya akalar mulki, illa dai kawai suna shirya bukukuwan al’ada masu kayatarwa. A wasu yankunan Indiyawa ma, irin wadannan masu kambin rikon ragamar al’umma bisa turbar gargajiya duk ya takaita ne wajen tarukan turakar turke ma’aurata.

Har yau din nan dai, Birtaniyawa na tinkaho da Sarauniya; Rashawa sun yi nadamar hallaka masu kambin sarautar Tsar (Sarkin ‘Za’), bayan juyin juya halin Bolshebik. Uwa-uba a yankunan Turai ba a rasa tsilli-tsillin masu rike tambarin jan ragamar al’umma bisa turbar gargajiyarsu. Su kuwa Larabawan Duniya, har yanzu ba su saki ba, domin mafi yawan manyan kasashensu suna karkashi ikon masu kambin gargajiya. Ga Hirohiton Japanawa da dai makamanansu.

Mu kuwa a Ifrikiyya manyan masu jan ragama da daularsu ta shafe tsawon zamani ba su wuce karamin lauje ba, wato Hassan na Moroko (magajinsa Muhammad) da Mswati mai tarin Adon-gari. Domin wadannan jiga-jigan al’umma daukacin fadin kasarsu suka gada, kuma suke da ikon juya akalar mulkin al’umma.

Shin ko akwai wani alfanu ne da za a ingizo mana da zarar mun yakice namu masu martabar, musamman yankunan Hau-hawar hawan sa, ba tare da sa-in-sa ba; ko kuwa a birnin Dabo ne ake son yin tsige-tsigen tsirin tsittsigen tsiron tsidahun tsandaurin tsigau?