✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rugumniyar rarumar ragama

Wa’adin mulkin karamin lauje ’Yan hamayya sun dauje Magabta ana kada musu jauje Marasa kishi anai musu jaje Muguwar manufa ta kuje   Masoya sun…

Wa’adin mulkin karamin lauje

’Yan hamayya sun dauje

Magabta ana kada musu jauje

Marasa kishi anai musu jaje

Muguwar manufa ta kuje

 

Masoya sun bararraje

Cikinsu har da mai saje

Suna kai-kawon a je-a je

Batutuwa ne a baje

A goge wa al’umma kaushin kauje

 

 

Butu-butun buruntun baza buje

Sai ai ta na-jan-je

Wai anje-anje

Ana ta bangaje-bangaje

Wasu har sun gwabje

 

Baba ya rataya gafaka

Sai fafutikar dinke baraka

Ko’ina sai ya taka

Al’umma dai ta ji a jika

Matakalar sabon salo aka taka

 

Iyakata dai kwatance

In yi ta zaro zance

Nagargaru kun san ayyukan dace

Kwararre ya zam fitacce

Babu waskiyar waskace-waskace

 

Rantsuwa ta ratsa

Miyagu sai a matsa

Masu himma a motsa

Ai gyaran karafunan tsatsa

Daukacin fagage a kutsa

 

Na ga jan cikin tsutsa

Masu hayagaga ban da nunin yatsa

Kar ku kitsa bahallatsa

Kowa dai ya samu tuwon datsa

Ai maganin ’yan dandatsa

 

Baba yai yunkurin aiki

Rikon ragama ba raki

Dattijo bai kukan aski

Ya dai yi furucin baki

Da karfinsa yake tattaki

 

Rantsuwar rikon ragama

Baba yai rummace

Kwado ne ba bambance-bambance

Ko ka-ce-na-ce

An tabbar da rikon makama

 

Da dai an ji jiki

Yanzu akwai karfin uwar-jiki

Sai dumfarar abin kirki

Banbamin bariki

Barden bindiga bai da burki

 

Rugumniyar rarumar ragama

Rahotannin rantsuwar raruma

Kar a ce Baba ya dan rurruma

Zangon karamin lauje ya kama

Mahukunta sun gyara zama

 

Fafatawa ba fantamawa

Tunkarar aiki ake takawa

Fafutikar farantawa

Al’umma su zam nunawa

Shugaba babu shakatawa

 

Ku kuwa

Gungun ’yan wawa

Lallai ana dada gargadawa

Dabarbarunku na dada birkicewa

Tuni an jinko damin da kuke tarawa

 

Saurayin-kirinki

Da an saki baki

Dagirgiri Dogari

Ya rage kai hari

Yanzu akwai rubirbidar na jaki

 

Baba a dage a ci maki

Garkamammun garada na shan tafkar tafki

Gundumin gwaramar gwabzar gwanki

’Yan kwadago na jiran taiki

Mangala ta antayo wa gayauna taki

 

Ayyukan ban mamaki

A daddale a harkokin mulki

Garken garakan naman girki

Gayaunar ganyayyaki

Tuwo miyar shukar shuwakar Shuwaki

 

Mu dai a kare mana mutunci

Tunda Baba ya hana cin hanci

Kishin kasa ya zam ba batanci

A kiyayi kulla munafunci

Sako-sakon sakacin sakarci

 

Kundumbalar kiyayya keke-da-keke

Karajin sarke-sarke

Kulle-kulle sun kuke

Kokiya ta harke

Kwakule-kwakulen hake-hake

 

Baban-burin-huriyya

Daga fari ka kai zuwa kurya

Kowace kwarya ta bi kwarya

A yasar da batun kiren karya

Talakawa sun yi juriya

 

Magabata na ta turjiya

Maketata na da kulle-kullen kulalliya

Munafukai na dada shirya murdiya

Mahankalata nai musu nuniya

Masana a sunce sasarin azargagiya

 

Rahotanin ruguntsumin ransuwar rugumniyar rarumar rakitar rikon ragama ya baibaye kafafen yada kakwazo na akwatunan baza batutuwa da masu wuntsila-gudi-gudin dodannin hotuna, wadanda suka  kyallara wa Haurobiyawa da daukacin fadin duniya yadda Baban-burin-huriyya ya rungumi rikon ragamar al’umma a wa’adin mulki karo na karamin lauje.

A wajen dandazon kamun ludayin wa’adin mulki na karamin lauje, Baban-burin-huriyya da mataimakinsa Usainin-Babajo da daukacin mukarraban gwamnatinsa, sun hallara, illa dai kawai tasgaron taron rashin halartar su ‘O’o da ‘U’u, su Baba-Ojo mai gonakin Otawa da Gudun-loko da Jonatantin-mulki da sauran shagabanin al’ummar Haurobiya, wadanda suka yi fafutikar dawo da Jam’iyya mai danboto da sanda jirge kan karaga, amma hakar kwakwarensu ba ta cimma na kwadi ba, ballantana ma su da gama-garin ’yan barandarsu su yi ta kwankwada, har su kwalfe, su kwankwade a makwalwa kwat, ba tare da sun rage wa kowa ko dis ba.

Shin bayan lamushe zababbakar zabukan shekara ta dubu karamin lauje da sili da manuniyar kasa da Baban-burin-huriyya ya yi, ya kuma yi RUGUMNIYAR RARUMAR RAGAMAR RIKON RAKUMMAN jan akalar tafiyar da harkokin mulkin Haurobiyawa, mene ne ya rage a tunkara, musamman jin cewa wannan shi ne zangon karamin lauje na karkare wa’adin mulkinsa?

Amasar dai ita ce, tunda wa’adin mulkin karamin lauje ya sanya’yan hamayya sun dauje har magabta sun sha kidin  juyin juya halin jauje, ga marasa kishi anai musu jaje, musamman jin cewa, muguwar manufarsu ta kuje. Don haka dai masoya aka bararraje  har ma da Malam mai saje ana ta kai-kawo a je-a je; batutuwa ne dai a baje. Babban muradinmu dai, daidai kan wannan gabar ba ta wuce ganin an goge wa al’umma kaushin kauje ba.

Haurobiyawa, tare da daukacin ’yan makarantar Dodorido da ke falle shafukan mujallu da makalu da jaridu, har ma da masu koyon watsattsaken fallen shafukan wagagen littattafan DARUSSAN DUNGUN DUMUINIYAR DODANNIN DUNIYA, ina matukar son in ari bakunanku in cumuimiye, in tattaune muku albashe-bashe mai lunkumemen lawashin laushi. Bisa wannan dalili na kashin kaina, ni ina matukar son ganin an aiwatar da dimbin ayyukan alherin da aka tattauna, tare da kulla yarjejeniya kansu yayin da Baban-burin-huriyya ya yi SHELAR SHATALE-TALE SHAN SHAYI, tare da GANGANKON GWANGWANIN GAREWANIN GAHAWA; uwa-uba ina da muradin ganin kafuwar MAKEKIYAR MAKARANTAR MAMA, amma da sharadin ba za a yi mana farfajiyar koyi-ka-koyar ko koyi-ka-karkatar mai tsandarewar tsawwalar tsula tsadar tsilla-tsilla tsokale damar marasa galihu, har ta kai ga ’ya’yan ALARAMMAN ALMAJIRAN AREWATAWA ba za su iya kutsa kurungunsu ba; kuma ina nan da muradina na ganin  kafuwar tsangayar alkafura da kundumbalar ninkayar iyo a kogin ilimu ta BABBAR BUKKAR BOKOKON BABAN-BURIN-HURIYYA, inda ’ya’yan Baba da Inna za su samu tarairaya da biyayya, bisa kumshiyar tanade-tanaden manhaja mara hajijiyar nusar da kyawawan ta’adun iyaye da kakanni. Lallai Baba ka tagaza, a agaza, musamman ma jin cewa Mama A’ISHATU FIL JAMI’A ta fita batun jar miya, ta samar wa su kolo da titibiri da gardin garada makoma a makarantarta, ko su ma sun dana SIRDIN SUDAN SADIDAN, su kuma rika kayatar da al’ummar Haurobiyawa tamfar dai sun fito daga kasaitattar kayatacciyar kasar Katar.

Mun dai karkare darasin wannan mako da neman agajin Mai-duka, Mai-kowa, Mai-komai don ya albarkaci wannan wa’adin karkare mulkin Baban-burin-huriyya, har mu samu mu kai ga gacin kawar da tashin-tashinar TSORO, har a fice daga yanayin nan na BA TSARO, SAI TSORO, tare da tabbacin cewa jami’an tsaro sun samu cikakken horon artabun angaje mana turka-turkar Haramta bobo da kwambon bokoko; a tarairayi ZULLUMIN ZALUNCIN ZALAMAR ZULLON ZINARUN ZAMAN-FARA; uwa-uba a tallafa wa Gwamna gwarangwam Mai-samari na Birnin Dikko, inda ba a dakon dakon mangalar aura, kan yadda zai tunkari matsalar KISISINAR KASHE-KASHEN KISSAR KISHIYOYIN KITSE-KITSEN KATSINTSINAWAR KASSARA al’umma. Yin haka ya zamo wajibi ganin cewa jihar da ake yiwa al’ummarta kisan mummuken sari-ka-noke ta Baba ce. Hasali ma har Magajin garin Daurama aka yi awon gaba da shi.

Lallai Baba ka kara daura damar, domin Jimamin jimirin jama’a na neman haifar musu da jante, amma dai da zarar an yunkura za a ci dunun darkakin dumuiniyar damuwar danniyar duniya. Mai-duka dai ya shige mana gaba a daukacin lamurranmu.