✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rumfar rufa-rufar ramuwar-fansa (2)

A muku-mukun makonnin wuccikewar watan runtuma rututun ruwa, kai har ma zuwa halin da muke ciki a watan Sambatun-Baba, Haurobiyawa sun yi ta ce-ce-ku-cen kai-kawon…

A muku-mukun makonnin wuccikewar watan runtuma rututun ruwa, kai har ma zuwa halin da muke ciki a watan Sambatun-Baba, Haurobiyawa sun yi ta ce-ce-ku-cen kai-kawon kokawa kan karon-battar Kudancin Ifrikiyya da bakin kasar. Mafi yawan masu takaddamar tattaunawar turka-turkar  tafka ta’asar tashin-tashinar taho-mu-gamar rayuwa da ya haifar da fatalin dimbin dukiya, sun yi ikirarin cewa ’yan kasar bakan-gizo sun yi wa al’umma BUGUN BABBAN BURGU, har ma da wankin BURGUJEJEN BABBAN BARGO, inda suka yi ta korafe-korafen kwafar kulafuci, wai bisa la’akari da ’yadda ’yan tsirari suka tsantsame, suka tsame tsamiyar hada-hadar arzikin kasar, alhali ’yan kasa na faman fantamawar fuffukar fatattakar fatara.

A wata ruwayar kuwa, cewa aka yi, Haurobiyawa ne ke  cefanar da kayan mamaye kwakwalwa, tare da badalar baddala bulalar bugun adon-gari, inda ake jefa azargagiyar zargin karo-karon wawancin, al’amarin da ka iya zama sanadin uwargida ta zamo uwargada, wato irin mai karairayar kantakaryar gwalangwason gwamuwar gwangwajewar gwanintar bara-gurbin burgar bulkarar burgewar bariki. Kai har ma labarin jinka wa jami’an tsaro na goriyar goro aka ce Haurobiyawan da ke zaune a Kudancin Ifrikiyya na dan tsuwurwurtawa.

Ko ma dai wacce aika-aikar Haurobiyawa mazauna Kudancin Ifirikiyya suka tafka har suka harzuka masu masaukinsu, ina ganin babban darasi a garemu, shi ne mu dauki izina. Kuma mu bijiro wa mahukunta muhimmancin bin kadin ta’adar al’ummar kasar nan, wadanda suka haure zuwa kasashen ketare.

Matsalar babakeren baki ya haifar da bangar Bakan-gizon bugun bargon burgu buguzum bazo-bazo, don nuna takaicin tsaurin tsirarun tsantsame tsamiya, inda aka ci gaba da Rawar roron ruge-rugen ruftawa rumfar rumurmutsar  romon ragon ramuwar-fansa.

Sanannen al’amari ne cewa, Haurobiyawa masu murgude-murguden mamular masa a wajen hargowar hasafin hau-hawar hawan-sa, su ne suka shahara da sagaraftu a kasar Sawun-diyyar Larabawa, kuma da zarar sun tafka ta’asa a kwanon tasa, sai kawai a tasa keyarsu gaba zuwa filin saukar tsuntsayen sama na Aminin sunce sasarin siyasar kewayen birnin Dabo, inda ba a dabo. Abin takaicin dai a nan shi ne, kafatanin kafta-kaftan kafofin lallaga laftun labarai na watsattsaken wallafe-wallafen wagagen littattafai da mujallu da makalu, har da masu kwakwazo a akwaku masu wuntsila gudi-gudin dodannin hotuna ba su cika bin kadin lamurarra yadda za a gane cewa ba Arewatawan Haurobiya ne suka tsuwurwurta mugun aiki ba, musamman ganin cewa akwai ’yan Niyyar-jari da al’ummar sauran sassan Yammacin Ifirikiyya da ke murguda muka-mukumin magana da yaren Hau-hau wajen hau-hawar hawan-sa ba tare da sa-in-sa ba. Sannan idan ta tabbata Haurobiyawan Haurobiya ne suka keta dokar wata kasa, har aka yiwo kasa-kasa da su, wajibi ne mahukunta su dan hora su, domin babban laifin a nan ba su kasance jakadu nagargaru ga kasar nan a lokacin da suka yi bulkalar balaguron buga-bugar babakere ba; idan kuwa ma ba Arewatawa ba ne, wajibi ne a nauyayya ninkayar niyyar nasihar nunin nusarwar illolin da ke tattare da aika-aikar afka wa wata kasa. Wannan ke nan.

Kuma daukacin al’ummar yankunan kasar nan sun yi kai-kawon sagaraftun sunkurun shigar limbu-limbun lambun Libiya, har zuwa lokacin da aka fara cinikin bayi aka tsahirta.

Mutanen da ke sagaraftun sunkurun shiga Turai na sane da cewa akwai Yaro-Baba da ke tafka irin ta shi/tata ta’asar a kasashen ketare. Mai biyan fura kuwa yana cukudi-cukudin camamar cin kudi ne a duk inda ya samu kansa, don ya more rayuwa, ya komo gida yana fankama, alhali an bar baya da kasurar kasaitar kasurgumar kurar kasa.

’Yan  makaranta wajibi ne a yi muku nunin nishadantarwar nuku-nukun nokewar nagargaru wajen kumbiya-kumbiyar tafka ta’asa a kasashen ketare, ta yadda a za a tantance tsaba da tsukuwar tsitakar tsikarar tsatsubar tsunburburar tsibirin tsuwwa tsibi-tsibi. Tun da dai an fasko bakin zaren zurmiyyar bakan-gizo, sai a daina yi mana gizo da dambarwar dukunkune-dukunkune, tun lamari na dan karami-karami kankane-kankane, har ya yi ta kasurar kundunbalar karfafa kone-kone, inda kasa da kasa ke ta yi wa juna gane-gane, ana shirin sa zaren damben dabarbarun danne-danne, ta hanyar  yada jita-jitar jirgiyar jigata da jagwalgwalon jangwale- jangwalen Jimurdar jimamin Jijjigar jugum-jugum jim a takaddamar  ja-in-jar jaye-jayen jajen juyin jarrabawar jarabta.

Haurobiyawa, ko kuna kai-kawon dawurwurin dumuiniyar dundumin yadda kuka tagaza wajen warware watangaririyar wafciyar wa-ka-ci-ka-tashin wariyar wuru-wuru da ta addabi Bukkar bakaken bakan-gizo ne? ta yiwu kuma godiyar maye aka yi muku. Sai dai in an bi ta barawo, a bi ta ma-bi sawu, ko? Shin mene ma dalilin da ya sanya kuka kukuta wajen shawo kan makarkashiyar murkushe Manin-Dela, zamanin da aka garkame shi a jarun?

A hir dinku Haurobiyawa! A yasar da HAYAGAGAR HARGAGIN HUTSANCIN HAUTSINEWAR HANTSEWAR HATSIN HANTSI!

Lallai mu yi fafutikar nusar da Shugaban kasar Kudancin Ifrikiyya, tare da daukacin al’ummar BABBAR BAKAR BAKAN-GIZO cewa, su yasar da irin wannan tunani nasu na kafa RUMFAR RUGUNTSIMIN RUMURMUTSAR ROMON RAGON RAMUWAR-FANSA, har ma da garkame-garkame JAJJAGA JIJJIGAR JAN-DAGAR JAN-KUBAR ZAMANIN ZUMUDIN ZAMAN ZOMON ZUMA, matukar suna son jin dadin bararrajewa baje-baje babu bangaje-bangajen jama’a. Idan na zomo ya yaji, to gangar jiki ta tsira. Al’amari mafi a’ala, shi ne, A duba MADUBIN MADABBA’AR MU’AMALAR MADIBAR MANIN-DELA, don kowa ya samu madogarar murmushin marmarin  mori-morin murmurewar mamular masar masoyan mutane.

Haurobiyawa, a ko’ina cikin sararin duniya kuka samu kurungunku, to ban da ramuwar gayya kan wani mummunan abin da aka tsuwurwurta don cutar da ku, sannan ku nusar da al’umma kyawawan halayen hankoron hada-hadar harhada halaliya, tare da hanzarin haramar haramta haramiya. Kuma a yi komai ba tare da duk wata kokowa ba.

Duk da cewa farfajiyar makarantar Dodorido da ke cikin Amintacciyar jaridar kasar Haurobiya na adawa da rangwadar ruguntsimin rawar roron ruge-rugen ruftawa rumfar rumurmutsar  romon ragon rufa-rufar rufin ramuwar-fansa, wadda aka tsuwurwurta a kasar Bakan-gizo, wajibi ne mu kyautatta dabi’a, mu zamanto masu da’a, miyagun ayyuka mu daina, in sun doso mu furta a’a, ta yadda a ko’ina muka samu kurungunmu a fadin duniyar nan za mu kasance cikin lullumin lumana lullum!

Sannan al’amari mafi a’ala, shi ne, a cusa manhajar maje haji ba tare da hajijiya ba, a daukacin harkokin koyon watsattsalke da falle shafukan mujallu da makalutun manufofin makalun wasikun wallafe-wallafen wagagen littattafai, wadda za ta yi wa Haurobiyawa hakikanin nunin ninkayar nayayya niyar shige da fice a kasashen ketare. Yin hakan ya zama dolen dole, musamman ma idan har ana son ka da a yi ta ketare dokokin kasashen duniya, kuma a karshe a karke da dawainiyar jigilar baki zuwa garuruwansu na haihuwa, har ma ana dan jnka musu wani abin hasafi, kamar yadda Madam mai dawainiyar Haurobiyawan kasashen ketare ta buge da  bikin dabiri ko dabarbarun birbiri, wajen jinka musu Hauro dubu tsayauwa bisa kafa guda da manuniyar sama. Mhm! MADAM ABUGE DA BIKIN DABIRI ke nan!

Ya dai zama tilas ga al’ummar Ifirikiyya kan kowa ya yi kira da karajin murya, wato cewa ai ta Tarayyar Ifrikiyya a wajen gangamin gayyatar gamayya gayya-gayya da kukuta kokarin kwazon  dakushe dafin kiyayya, ta hanyar  nuna sanayyar saisaita sungumemen sasarin soyayya, a wajen tunkarar turmuttsitsin taron tallafin tarairayar tarayya.