Kungiyar kamfe na dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP (PPCO) ta bukaci sabon Sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya na riko, AIG Abubakar Adamu Muhammed da ya tabbatar sahihancin aikin hukumar ‘yan sandan Najeriya.
Daraktan sadarwa na kungiyar Kola Ologbondiyan ya bukaci sabon shugaban ‘yan sandan Najeriya da ya yi watsi da shirin da wasu ‘yan siyasa ke da shi na yin magudin zaben 2019.