✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Samar da fitilu a manyan titunan Legas na rage yawan barayi Inji Gwamna Fashola

Gwamnan Jihar  Legas,  Mista Babatunde Raji Fashola  ya kaddamar  da  fitilun titi a  tsohuwar  gadar Carter Bridge, wadda ta hada dukan sassan Legas, wato Lagos…

Gwamnan Jihar  Legas, Babatunde Raji Fashola ya buxe fitilun gadar Carter BridgeGwamnan Jihar  Legas,  Mista Babatunde Raji Fashola  ya kaddamar  da  fitilun titi a  tsohuwar  gadar Carter Bridge, wadda ta hada dukan sassan Legas, wato Lagos Island da Lagos Mainland, wadda aka gina  tun a  shekarar  1901 kuma  a shekarar 1973 aka sake mata kwaskwarima.
An samar da turakun fitilu har 412 daga farko har karshen gadar, baya ga wadanda  aka samar a gefen masu tafiya da kafa da kuma hasken da ke raba  titin, lamarin da ya haskaka duk sassan Ijora Olopa da Iddo Terminus da EbutewEro.
A jawabinsa lokacin kaddamar  da  fitilun, Gwamna Fashola ya ce  samar da  wadataccen hasken lantarki  a sassan  jihar  na daya daga  cikin  abin da  gwamnatin jihar  ta yi  wa  jama’ar  alkawari,  duk da yake ba  aikinta ba ne. Ya ce samar da fitilun, zai agaza wajen rage yawan barayi,  kana ya samar  da  karin zirga-zirgar ababen hawa a yankunan.
Gwamna Fashola ya ce samar da wadannan fitilu, shi ne aiki irinsa na farko da  hukumar  samar  da lantarki ta jiha  mai  zaman kanta  ta  samar,  kuma  tuni  har  an fara  aikin  fadada  shi zuwa  wurare  kamar asibitoci  hudu  da ke  yankin da makarantu 14 da wuri biyu  na samar  da  ruwan  sha  ga  wani  sashen jihar da kotuna  2 da kuma titi mai tsawon kilomita 30.
Gwamnan ya ce  gwamnati  ta  gama nata,  yanzu ya rage  ga  mutanen  gari,  musamman wadanda  ke  makwabtaka  da wadannan  wuraren su sa  ido  su kula  da shi  tamkar nasu.
Ya ce daga  cikin abubuwan da  ke kawo  lalacewar  kayan gwamnati  shi ne  yadda  wasu ’yan kasa kan rika yi masa  rikon sakainar  kashi   ta  nuna  halin ko-oho. Ya kamata  a ce  an wuce wannan yanayin domin al’umma kodayaushe  kara  wayewa  take  yi. Don haka ya kamata jama’a  su kula da wadannan fitilu, wadanda da  kudinsu  ne  aka samar  da su.