Allah Ya yi wa tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP Sanata Babayo Garba Gamawa rasuwa.
Ya rasu ne bayan gajeruwar rasahin lafiya a asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) jihar Bauchi jiya Juma’a, ya rasu ya nada shekara 53.
Kamar yadda mai magana da yawun marigayin Isah Garba Gadau, ya sanarwa wakilinmu ta wayar tarho.