A karon farko a cikin shekara 13 kasar Senegal ta kai matakin Semi Fainal a gasar cin Kofin Afirka.
Dan kwallonsu Gueye ne ya jefa kwallo daya tilo a ragar Benin wanda hakan ya ba su damar kaiwa wannan matsayi.
Rabon da Senegal ta kai wannan mataki shekara 13 ke nan da suka gabata.
Sadio Mane, dan kwallon Liberpool da ke Ingila yana daga cikin ’yan kwallon da ke yi wa Senegal wasa a gasar.