Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya dage ziyarar kaddamar da aiki ta kwana daya da zai kai jihar Imo a yau Talata.
Shugaban zai kaddamar da wasu sabbin ayyuka da gwamnatin jihar Imo ta yi.
Sakataren watsa labaran Gwamnan Jihar Imo Sam Onwuemeodo ne ya bayyanawa manema labaran hakan a yau, ya ce an dage ziyarar ne saboda shugaban kasa yana shirin dawowa daga kasar Saudiyya bayan yin Umrah.