✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji da ‘yan shi’a sun sake yin arangama a Abuja

Ana tsammanin wasu ‘yan shi’a sun rasu yayin da wasu kuma suka jikkita bayan arangamar da jami’an tsaro suka yi da ‘yan shi’a bayan ‘yan…

Ana tsammanin wasu ‘yan shi’a sun rasu yayin da wasu kuma suka jikkita bayan arangamar da jami’an tsaro suka yi da ‘yan shi’a bayan ‘yan shi’an sun yi kokarin shiga Abuja a ci gaba da tattaki da suke yi.

Lamarin ya faru ne a daidai mashigar Karu da ke Abuja inda ‘yan kungiyar ta IMN suke tattaki da misalin karfe biyar na yamma.

Bayanai sun suna cewa sojoji sun bude wuta ne ga ‘yan shi’a din bayan sun yi kokarin wucewa ta shinge da sojojin suka saka domin hana su shigowa Abuja.