Rundunar sojojin Najeriya ta ce, dakarunta sun dakile harin ‘yan Boko Haram a karamar hukumar Michika jihar Adamawa.
Kakakin rundunar sojojin Najeriya Kanal Sagir Musa ne ya sanar da hakan, inda ya ce ‘yan Boko Haram sun yi yunkurin kai hari a garin Michika amma daga bisani sojojin suka yi nasarar dakile harin.
`Yan kungiyar sun yi yunkurin tserewa lokacin da suka shirya ke harin amma dakarun suka bude masu wuta wanda hakan yasa suka ci galaba akan su.