Rundunar hadaka ta dakarun kasashe da ke yaki da ‘yan Boko Haram a yankin tafkin Chadi, MNJTF, sun kashe mayakan Boko Haram 39 tare da kwato makamai masu yawa a hannun su, a yayin arangamar sojoji 20 sun samu raunuka.
Kakakin rundunar sojojin Kanal Timothy Antigha, ya tabbatar da aukuwar lamarin lokacin da yake ganawa da manema labarai jiya Laraba a Abuja.
Kanal Timothy, ya ce an kashe maharani ne a yankin Cross Kauwa jihar Borno ranar Talata yayin da wadanda aka raunata yanzu haka suke asibiti suna jinya.