✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun hana mu binne ’yanuwanmu- Shi’a

’Yan shi’a sun yi zargin cewa sojoji sun hana su amfani da makabartarsu domin binne ’yan uwansu da ake kashe a Abuja. Daya daga cikin…

’Yan shi’a sun yi zargin cewa sojoji sun hana su amfani da makabartarsu domin binne ’yan uwansu da ake kashe a Abuja.
Daya daga cikin mambobin kungiyar mai suna Mohammed Ibrahim Gamawa ne ya fada hakan a lokacin day a jagoranci tawagar ’yan shi’a din zuwa ofishin Media Trust mai buga jaridar Daily Trust da Aminiya a Abuja.
Ya bayyana cewa a lokacin da suka kai gwarwakin mutum 43 da aka kashe musu a Abuja domin su binne su, sai sojoji suka fada musu an ba su umarnin aka kada su barsu.