✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojojin Najeriya da Kamaru sun kashe mahara 27

Rudunar sojojin hadin gwiwa na Najeriya da Kamaru sun yi nasarar kashe ‘yan Boko Haram 27 a wani samame da suka kaiwa `yan kungiyar, sojojin…

Rudunar sojojin hadin gwiwa na Najeriya da Kamaru sun yi nasarar kashe ‘yan Boko Haram 27 a wani samame da suka kaiwa `yan kungiyar, sojojin sun lalata abubuwan hawa tare da kwato makamai masu yawa na maharan  a Borno.

Mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar sojojin Najeriya Kanal Sagir Musa ne ya tabbatar da hakan a yau Litinin.

Kanal Sagir, ya ce rundunar ta dakile shirin ‘yan Boko Haram a Arewacin Wulgo da Tumbuma, Chikun Gudu da kauyen Bukar Maryam.