An zabi Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal, a matsayin sabon hugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP.
Sabon shugabana ya ce kungiyar zata yi aiki tare da kwamitin gudanarwar jam’iyyar PDP wajen inganta jam’iyyar tare da karfafa dimokuradiyya a Najeriya.
Gwamna Tambuwal wanda zai gaji takwaransa na jihar Bayelsa Seriake Dickson wanda wa’adinsa ke karewa nan da mako biyu masu zuwa.
Tambuwal ya bayyana haka ne a lokacin bude taron kwamitin zartaswar jam’iyyar karo na 88 a yau Litinin a Abuja.