Sakamakon zubar dusar kankara da tsanantar sanyi a Jihar Logar da ke Afghanistan, an bayar da rahoton rasuwar mutum biyar da ke zaune a wani sansanin masu neman mafaka.
Kakakin Fadar Gwamnan Logar, Didar Ahmad Labang ya fada wa manema labarai cewa, an shafe tsawon kwanaki ana ta ruwan dusar kankara a jihar wanda hakan ya janyo tsananin sanyi.
Labang ya ce muni tare da tsanantar sanyin ne suka haddasa rasuwar mutum biyar da ke zaune a sansanin masu neman mafaka na tsakiyar Logar.
Ya ce sakamakon sanyin an dakatar da zirga-zirgar ababen hawa a gundumomi da dama na Jihar Logar.