Tsohon Ministan Lafiya na Najeriya, Dakta Haliru Alhassan ya rasu ranar Lahadi da misalin karfe 12 na rana bayan gajeruwar rashin lafiya.
Dakta Haliru Alhassan ya rasu yana da shekara 66.
Dakta Halliru ya yi fama da ciwon suga kafin rasuwarsa. Ya rasu ya bar mata daya da yara hudu.
- Alkalin da ya soke zaben Abiola ya rasu
- Dage dokar zaman gida: Kare kai na yi wa mazauna Abuja wahala
- Yayan mahaifin gwamnan Sakkwato ya rasu
- Tsohon gwamnan Sakkwato Garba Nadama ya rasu
Marigayi Halliru abokin Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar, ne tun suna yara.
Iyalan marigayin sun ce za a binne tsohon Ministan ne a makabartar Hubbaran Shehu da ke jihar Sakkwato.