Tsohon Ministan tsaro kuma Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Farfado da Arewa maso Gabas, Theophilus Yakubu Danjuma ya yaba wa matakin da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa Kiristoci daga jam’iyyun siyasa daban-daban musamman PDP da APC a Jihar Nasarawa suka dauka na don fahimtar juna a tsakaninsu a farkon wannan makon.
Theophilus Danjuma wanda shi ne shugaban taron, ya ce taron shi ne irinsa na farko da aka gudanar a jihohin kasar nan. Ya ce ba shakka hakan ya nuna karara cewa ‘yan siyasa kiristoci a Jihar Nasarawa sun san abin da suke yi, idan aka yi la’akari da bambance-bambancen siyasa dake tsakaninsu, suka ga ya dace su gudanar da taron don su fahimci junansu da hakan a cewarsa zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya tsakaninsu da ma sauran ‘yan siyasa daga sauran addinai a jihar.
Danjuma ya kuma bukaci sauran ‘yan siyasa kiristoci su yi koyi da abin da wadannan ‘yan siyasa kiristoci a jihar suka yi, don tabbatar da zaman lafiya da kauna tsakaninsu baki daya. Ya kuma bukaci sabbin shugabannin kungiyar kiristoci a jihar da su tabbatar sun gudanar da harkokin kungiyar cikin gaskiya da rikon amana don tabbatar da dorewar cigaba da ake samu a jihar musamman na hadin kawunan al’ummar kiristoci da ma wadanda ba kiristoci ba a Nasarawa.
Shi ma a jawabinsa Mataimakin Gwamnan Jihar, Mista Silas Ali Agara wanda ya sha kaye a zaben fid da gwani na gwamna a APC a jihar, ya bayyana cewa jiga-jigan ‘yan siyasa kiristocin da sauran kiristoci masu ruwa da tsaki a siyasar jihar sun ga dacewar su shirya taron don tunatar da junansu cewa kodayake kowannensu na da nasa ra’ayin siyasa, amma kada su manta cewa dukkansu daya ne a gun Isah Almasihu.
Shi ma a nasa bangaren sabon shugaban kungiyar kiristocin jihar da aka rantsar a yayin taron, Bishop Joseph Masin ya yaba wa hangen nesan da a cewarsa ‘yan siyasa kiristoci daga dukkan jam’iyyu a jihar suka yi, inda ya shawarce su da su kafa wata kungiya ta Kiristoci ‘yan siyasa a jihar da kasa baki daya don kara inganta wannan zumunci da fahimtar juna a tsakaninsu.