✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Wadanda suka kamu da Coronavirus a Najeriya sun zama 51

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta sanar da karin mutum biyar da suka kamu da cutar Coronavirus a kasar. An samu…

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta sanar da karin mutum biyar da suka kamu da cutar Coronavirus a kasar.

An samu karin mutane biyu a Yankin Babban Birnin Tarayya, da biyu a Legas, sai kuma guda a Jihar Ribas.

Hakan ya sa adadin mutanen da suka kamu da cutar a Najeriya ya kai 51.

A ranar Laraba kadai an samu karin mutane bakwai da suka kamu da cutar.

A yanzu haka an tabbatar da akwai masu dauke da cutar a jihohi kamar haka: mutum 32 a Jihar Legas, a Yankin Babban Birnin Tarayya akwai mutum 10, a Jihar Ogun mutum uku, sai kuma jihohin Ekiti daya, Oyo daya, Edo daya, Bauchi daya, Osun daya, da kuma Ribas daya.